RUGUNTSUMI PART 19..12/2/2017
Yana kokarin rungumeta tana dukan sa a kirji,
tana kuka tana fadin ya fitar mata a daki.
Wani Kukan ne mai tafasa zuciya ta fashe dashi
“Na tsaneka JAN banason ganinka! na tsaneka
banason ganinka!! Na tsaneka bana son
ganinka!!!” Abinda take maimatawa kenan tana
wani irin kuka mai tsuma zuciya, gaba daya JAN
ya rude, ba abinda ke masa dadi musamman
ganin Hajiya tana masa wannan kukan, tabbas a
haihuwar wuri ta haifeshi, ga kudi Allah ya
bata,
amma itace take masa wannan kukan kamar
ranta zai fita,
Sam batajin rarrashin da yakeyi, sai fadar take
ta tsaneshi, wannan kalmar ba karamin wargaza
masa tunani takeyiba,
” ka sakeni Jalal bana son ganin ka”
Wata irin tsawa ya daka mata wacce ta aiko
mata da mala’ikar natsuwa, tuni ta natsu tayi
shiru, ta lafee a kirjinsa, a hankali ya fara
bubbuga bayan ta kamar ana rarrashin yaro
karami.
A hankali taji natsuwa tana sauko mata, yaci
gaba da mata waiwayi, ko minti uku ba’ayiba sai
bacci ya d’auketa ba karamin wuya tasha ba,
tsayawa yayi ya kare mata kallo, tabbbas
wannan matar akwai kishin bala’ee, sai kace ta
gansu turmi tabarya, yanzu ta masa haka inaga
ta sami labarin Hany, guntun tsaki yaja, a
hankali ya zame jikinsa ya janyo pillow ya daura
mata ya fito dakin, ko minti biyar ba’ayi ba sai
gata ta tashi kamar an tsikareta,
Sai kace wacce tayi wani mafarki, ko ina ta
zagaye bata ganshi ba, chan ta hangoshi hanyar
kitchen yana waya, kuma ga dukkan Alamu
wayar ta munafunci yakeyi, zuciyarta take cewa
taje gurinsa wata zuciyar na ce mata kada kije ki
jiyo bakin ciki, a hakan ta tsaya amma wayar
taki karewa, bugun zuciyarta yake daduwa duk
lokacinda ta waigoshi, sai taga kamar ma yana
dariya, a hankali ta tashi ta shigo kitchen din
kalmar da ta fado kunnen tace ta nemi ta
wargaza mata kwakwalwa.
“Wallahi Zan iya rabuwa da ita koda zan
dawwama cikin bakin cikine..!!!
tana kuka tana fadin ya fitar mata a daki.
Wani Kukan ne mai tafasa zuciya ta fashe dashi
“Na tsaneka JAN banason ganinka! na tsaneka
banason ganinka!! Na tsaneka bana son
ganinka!!!” Abinda take maimatawa kenan tana
wani irin kuka mai tsuma zuciya, gaba daya JAN
ya rude, ba abinda ke masa dadi musamman
ganin Hajiya tana masa wannan kukan, tabbas a
haihuwar wuri ta haifeshi, ga kudi Allah ya
bata,
amma itace take masa wannan kukan kamar
ranta zai fita,
Sam batajin rarrashin da yakeyi, sai fadar take
ta tsaneshi, wannan kalmar ba karamin wargaza
masa tunani takeyiba,
” ka sakeni Jalal bana son ganin ka”
Wata irin tsawa ya daka mata wacce ta aiko
mata da mala’ikar natsuwa, tuni ta natsu tayi
shiru, ta lafee a kirjinsa, a hankali ya fara
bubbuga bayan ta kamar ana rarrashin yaro
karami.
A hankali taji natsuwa tana sauko mata, yaci
gaba da mata waiwayi, ko minti uku ba’ayiba sai
bacci ya d’auketa ba karamin wuya tasha ba,
tsayawa yayi ya kare mata kallo, tabbbas
wannan matar akwai kishin bala’ee, sai kace ta
gansu turmi tabarya, yanzu ta masa haka inaga
ta sami labarin Hany, guntun tsaki yaja, a
hankali ya zame jikinsa ya janyo pillow ya daura
mata ya fito dakin, ko minti biyar ba’ayi ba sai
gata ta tashi kamar an tsikareta,
Sai kace wacce tayi wani mafarki, ko ina ta
zagaye bata ganshi ba, chan ta hangoshi hanyar
kitchen yana waya, kuma ga dukkan Alamu
wayar ta munafunci yakeyi, zuciyarta take cewa
taje gurinsa wata zuciyar na ce mata kada kije ki
jiyo bakin ciki, a hakan ta tsaya amma wayar
taki karewa, bugun zuciyarta yake daduwa duk
lokacinda ta waigoshi, sai taga kamar ma yana
dariya, a hankali ta tashi ta shigo kitchen din
kalmar da ta fado kunnen tace ta nemi ta
wargaza mata kwakwalwa.
“Wallahi Zan iya rabuwa da ita koda zan
dawwama cikin bakin cikine..!!!
Comments
Post a Comment