RUGUNTSUMI PART 23..15/2/2017
“ATM card ta miko masa ya saka aljihu,
“Okay Na fadi nawa saura naki”
tashi tayi ta fuskanceshi.
Sai Kuma ta kasa magana, ya dawo ya tallabo
fuskanta, sabida ya gane cewa ba abinda yake
tunani bane, wani abin ne daban take son fada
mishi, Amma Kuma ta kasa,
“Tell me mana! Nasan akwai zance cikin
bakinki,”
Kallon sa tayi jiki a mace,
“Jalal dama…”
Sai Kuma ta sakeyi tayi shiru,
“Dama me? Dama akwai abinda ba zaki iya
fada min ba?”
Kara matsowa da ita yayi jikinsa,
“Dama Jalal I’m pregnant”
Ta fada hadi da runtse Ido tana jiran amsarsa.
Numfashinsa ne kawai bai dauke ba, komai
nasa tsaya wa yayi Chak.!
Cikin rashin kuzari ya dago ido ya kafa mata,
dugar da kanta tayi kasa,
“How? Ya Hakan ta faru Hajiya? Ya zaki bari ki
dauki ciki?”
Dago Kai tayi cikin salon kissa, duk da cewa
cike take da fargabar mi zai faru amma kuma
sai ta dake sosai,
“Wallahi ban san yanda hakan ta faru ba,
saboda ina shan magani duk wata, bayan allurar
da nayi ta shekara biyar.”
Girgiza kansa yayi,
“No Hajiya, No…. Da kina shan maganin da
bazai shigaba, wallahi ki sani bazan taba
haihuwa ba Aure ba, No” .
Abinda ya rika nanatawa kenan,
“Jalal naso muyi Aure tun hakan bata faru ba,
amma Kuma Sai Allah yayi nashi ikon”
“Allah yayi nashi ikon ko ke kikayi naki ikon?
Hajiya da gangan kika dauki wannan cikin sabida
kina son Na Aure ki, sannan idan har kina ganin
sabida wannan cikin zaisa na aureki kinyi
kuskure,”
Ya fada yana nunata da yatsa, duk da yanajin
radadin yin hakan,
Mike wa yayi tsaye ya bata baya,
“Idan har kika ga na Aure ki, to ki tabbatar da
sai an zubar da wannan cikin.”
Bai tsaya komai ba ya wuce dakinsa, ya barta
nan zaune,
Zuciyar ta ce take bugawa.
Ta tuna abinda likitanta ya gaya mata sgekaru
uku da suka wuce.
“Hajiya idan har kika bari ciki ya shigeki to
lallai Sai kin haifeshi, saboda mahaifarki tayi
yaushi sosai, idan har akayi kokarin zubar da
cikin zaki iya rasa rayuwarki gaba daya, kinga
dai yanda kika sha wannan karon, kiris ya rage
ki harba kiyama, saboda haka Ina dada
shawartar ki kada ki kuskura kiyi kuskuren
daukar ciki, idan kinyi Kuma to ki shirya
haihuwarsa saboda bazai ciruba”
Numfashi ta sauke, a hankali ta fada tare da
shafa cikin,
“Jalal bazan zubar da rayuwa ta ba,”
Ta kara shafar cikin,
Wannan shine ciki Na farko da taji tana so Kuma
tana kauna a rayuwarta,
Hajiya tayi ciki kala kala, tana zubarwa, hatta
haifaffen ciki ta taba yarwa saboda tsabar
ta’addancinta.
Wasu hawaye ne suka gangaro mata lokacin da
ta tuna margayin mijin ta.
“Maman Ummi dan darajar Allah kada ki sake
zubar min da ciki, zanyi farin ciki idan har
kikayi allura ta hana daukar ciki bawai ki rika
zubar min da yayaba, inason kayana.”
Hararan sa tayi, hadi da masa tsaki,
“Wallahi bazanyi allurar komai ba Kuma duk
ciki ya shiga idan har banso shigar sa ba, to
kuwa zan zubar da banza, saboda ba dan
haihuwa nake zaune gidan nan ba, bazan zauna
yara su mayar dani tsohuwar karfi da yajiba.”
“Maman Ummi ki….”
Tsawa ta daka masa, tuni ya nemi hanyar barin
dakin, bakin kofa ya tsaya,
“Idan har kika kara zubar min da ciki Allah ya
saka min duniya da lakhira, sannan Allah ya
hanaki ciki lokacin da kike neman sa, ko ya baki
cikin lokacin da maishi baya bukatar sa,”
Ya sa kai ya fita wannan tafiyar ita tayi
sanadiyar mutuwar mijinta, Kuma ita sanadin
arzikinta, saboda kudin diyyar da aka bata nashi
sunada yawa tunda jirgine ya kife dashi.
Taci gaba da kukan ta,
Yau gata da mafi soyuwar ciki Amma maishi
baya so, lallai addu’ar tsohon mijinta ta karbu,
Haka dai taci kukanta har ta gode Allah, nan
barci yayi awon gaba da ita…
“Okay Na fadi nawa saura naki”
tashi tayi ta fuskanceshi.
Sai Kuma ta kasa magana, ya dawo ya tallabo
fuskanta, sabida ya gane cewa ba abinda yake
tunani bane, wani abin ne daban take son fada
mishi, Amma Kuma ta kasa,
“Tell me mana! Nasan akwai zance cikin
bakinki,”
Kallon sa tayi jiki a mace,
“Jalal dama…”
Sai Kuma ta sakeyi tayi shiru,
“Dama me? Dama akwai abinda ba zaki iya
fada min ba?”
Kara matsowa da ita yayi jikinsa,
“Dama Jalal I’m pregnant”
Ta fada hadi da runtse Ido tana jiran amsarsa.
Numfashinsa ne kawai bai dauke ba, komai
nasa tsaya wa yayi Chak.!
Cikin rashin kuzari ya dago ido ya kafa mata,
dugar da kanta tayi kasa,
“How? Ya Hakan ta faru Hajiya? Ya zaki bari ki
dauki ciki?”
Dago Kai tayi cikin salon kissa, duk da cewa
cike take da fargabar mi zai faru amma kuma
sai ta dake sosai,
“Wallahi ban san yanda hakan ta faru ba,
saboda ina shan magani duk wata, bayan allurar
da nayi ta shekara biyar.”
Girgiza kansa yayi,
“No Hajiya, No…. Da kina shan maganin da
bazai shigaba, wallahi ki sani bazan taba
haihuwa ba Aure ba, No” .
Abinda ya rika nanatawa kenan,
“Jalal naso muyi Aure tun hakan bata faru ba,
amma Kuma Sai Allah yayi nashi ikon”
“Allah yayi nashi ikon ko ke kikayi naki ikon?
Hajiya da gangan kika dauki wannan cikin sabida
kina son Na Aure ki, sannan idan har kina ganin
sabida wannan cikin zaisa na aureki kinyi
kuskure,”
Ya fada yana nunata da yatsa, duk da yanajin
radadin yin hakan,
Mike wa yayi tsaye ya bata baya,
“Idan har kika ga na Aure ki, to ki tabbatar da
sai an zubar da wannan cikin.”
Bai tsaya komai ba ya wuce dakinsa, ya barta
nan zaune,
Zuciyar ta ce take bugawa.
Ta tuna abinda likitanta ya gaya mata sgekaru
uku da suka wuce.
“Hajiya idan har kika bari ciki ya shigeki to
lallai Sai kin haifeshi, saboda mahaifarki tayi
yaushi sosai, idan har akayi kokarin zubar da
cikin zaki iya rasa rayuwarki gaba daya, kinga
dai yanda kika sha wannan karon, kiris ya rage
ki harba kiyama, saboda haka Ina dada
shawartar ki kada ki kuskura kiyi kuskuren
daukar ciki, idan kinyi Kuma to ki shirya
haihuwarsa saboda bazai ciruba”
Numfashi ta sauke, a hankali ta fada tare da
shafa cikin,
“Jalal bazan zubar da rayuwa ta ba,”
Ta kara shafar cikin,
Wannan shine ciki Na farko da taji tana so Kuma
tana kauna a rayuwarta,
Hajiya tayi ciki kala kala, tana zubarwa, hatta
haifaffen ciki ta taba yarwa saboda tsabar
ta’addancinta.
Wasu hawaye ne suka gangaro mata lokacin da
ta tuna margayin mijin ta.
“Maman Ummi dan darajar Allah kada ki sake
zubar min da ciki, zanyi farin ciki idan har
kikayi allura ta hana daukar ciki bawai ki rika
zubar min da yayaba, inason kayana.”
Hararan sa tayi, hadi da masa tsaki,
“Wallahi bazanyi allurar komai ba Kuma duk
ciki ya shiga idan har banso shigar sa ba, to
kuwa zan zubar da banza, saboda ba dan
haihuwa nake zaune gidan nan ba, bazan zauna
yara su mayar dani tsohuwar karfi da yajiba.”
“Maman Ummi ki….”
Tsawa ta daka masa, tuni ya nemi hanyar barin
dakin, bakin kofa ya tsaya,
“Idan har kika kara zubar min da ciki Allah ya
saka min duniya da lakhira, sannan Allah ya
hanaki ciki lokacin da kike neman sa, ko ya baki
cikin lokacin da maishi baya bukatar sa,”
Ya sa kai ya fita wannan tafiyar ita tayi
sanadiyar mutuwar mijinta, Kuma ita sanadin
arzikinta, saboda kudin diyyar da aka bata nashi
sunada yawa tunda jirgine ya kife dashi.
Taci gaba da kukan ta,
Yau gata da mafi soyuwar ciki Amma maishi
baya so, lallai addu’ar tsohon mijinta ta karbu,
Haka dai taci kukanta har ta gode Allah, nan
barci yayi awon gaba da ita…
RUGUNTSUMI PART 23..15/2/2017 http://mubarakadamu.blogspot.com/2017/02/ruguntsumi-part-231522017.html
ReplyDelete